1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Boko Haram ta farwa masu zabe

Muntaqa AhiwaMarch 28, 2015

'Yan bindiga sun kai hare-hare a rumfunan zabe a Najeriya

https://p.dw.com/p/1Eyzc
Boko Haram Kämpfer
Hoto: picture alliance/AP Photo

Rahotanni daga Najeriya, na cewa 'yan bindiga da ake zargin mayakan Boko Haram ne sun afkawa runfunan zabe a wasu yankunan arewa maso gabashin kasar.

Bayanai sun ce maharan sun buda wuta a kan masu zabe a kauyukan Birin Bolawa da kuma Birin Fulani da ke yankin Nafada a jihar Gombe inda suka kashe akalla mutane biyu.

Wani jami'in zabe da bai so a bayyana sunansa ba, ya shaidawa kamfanin labaran Faransa AFP cewa, sun yiwo 'yan bindigan na cewa ''ai mun riga mun gargade ku kan zabe''.

Cikin wani faifan bidiyo a watan jiya, shugaban mayakan Boko Haram Abubakar Shekau, ya yi barazanar kawo tsaiko ga zabukan na Najeriya.