1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Boko Haram ta kai hari a gabashin kasar Nijar

Salissou BoukariJune 18, 2015

Hukumomin tsaro a Jamhuriyar Nijar sun tabbatar da wani hari da 'yan kungiyar Boko Haram suka kai a wasu garuruwa guda biyu na jihar Diffa da ke gabashin kasar.

https://p.dw.com/p/1FjHa
Notunterkünfte bei Diffa Niger
Hoto: DW/Larwana Malam Hami

Rahotanni daga Jamhuiriyar Nijar na cewa 'yan kungiyar Boko Haram sun kai hari a daren Laraba a wasu garuruwa guda biyu da ke cikin jihar Diffa a gabashin kasar ta Nijar, inda suka kashe mutane akalla 30. Wannan dai shi ne karo na biyu da 'yan kungiyar ta Boko Haram ke kai hari a wajan kasar Najeriya cikin mako guda, bayan harin da suka kai a ranar Litinin a birnin Ndjamena na kasar Chadi, wanda ya yi sanadiyyar rasuwar mutane 34.