1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Boko Haram ta kashe sojoji a Borno

Abdul-raheem Hassan
March 16, 2020

Dakarun gwamnatin Najeriya shida sun mutu a wani sabon harin kwantar bauna da mayakan jihadi suka kaddamar kan ayarinsu a kusa da kauyen Mayanti da ke kusa da iyaka da Kamaru.

https://p.dw.com/p/3ZUvp
Symbolbilder Niger Armee
Hoto: Getty Images/AFP/I. Sanogo

Kamfanin dillancin labarun Faransa AFP ya samu tabbacin faruwar harin yayin da sojojin ke hanyar zuwa kusa da garin Banki.

Duk da ikirarin gwamnatin Najeriya da rundunar tsaron kasar na samun galaba kan mayakan Boko Haram, Majalisar Dinkin Duniya na damuwa kan yadda maharan ke cigaba da dauki ba dadi da kuma halaka mutane.