1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Boko Haram: Yara miliyan daya ba sa karatu

Ahmed SalisuDecember 22, 2015

Rikicin Boko Haram da wasu kasashe a yammacin Afirka ke fama da shi musamman Najeriya ya hana yara kimanin miliyan guda zuwa makaranta.

https://p.dw.com/p/1HRTr
Kinder gehen zur Schule in Abuja Nigeria Archiv 22.09.2014
Hoto: picture-alliance/epa/T. Nwosu

Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya ya ce rashin zuwa makaranta da yara ke yi a arewacin Najeriya sakamakon rikicin Boko Haram ka iya taimakawa wajen haifar da karin masu tsaurin kishin addini.

Asusun dai ya bayyana hakan ne a wani sabon rahoto da ya fidda kuma hakan inji jami'in da ke kula da asusun a yammaci da tsakiyar Afirka Manuel Fontaine in yaran ba sa zuwa makarata, 'yan ta'adda ka iya sace su sannan su sanyasu a turbar da ba ta dace ba.

Kimanin makarantu 2000 ne wannan rikici ya sanya aka rufe su a Najeriya da Nijar da Kamaru da Chadi, yayin da dalibai sama da miliyan guda ba sa zuwa makaranta kana daruruwan malamai suka rasa ransu sakamakon rikicin.

Hukumomi a Najeriya dai sun lashi takobin kawo karshen tada kayar baya ta kungiyar ta Boko Haram a Najeriya. Rikicin dai ya yi sanadin rasuwar dubban mutane.