1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bukukuwan karamar Sallah a Nijar

Zainab Mohammed AbubakarJuly 5, 2016

Tun da maraicen ranar Litinin ce majalisar musuluncin kasar ta sanar da ganin jinjirin watan Shawwal a garuruwa dabam-dabam, wanda ya kawo karshen azumin watan Ramadan.

https://p.dw.com/p/1JJU3
Eid Al Fitr in Zinder, Niger
Hoto: DW/L. Malam Hami

A wannan Talatar ce aka gudanar da hawan idin karamar Sallah da ake kira Sallar Azumi a birnin Damagaram, inda dubban jama’a suka halarci filin idi.

Kazalika sauran jama'a a wasu garuruwa kamar birnin Yamai da Maradi da Gaya da makamantansu an gudanar da bukin Sallar lami lafiya.

Bayan wanan hutuba ce dai mai alfarma sultan na Damagaram Alhaji Abubakar Sanda ya yi kira ga al'ummar musulmi da su gudanar da rayuwa mai abun koyi ga sauran jama'a.

A can ma dai jahar Diffa mai fama da rikicin kungiyar Boko Haram rahotanni na cewar al’umma sun gudanar da hawan idin lami lafiya cikin tsauraran matakan tsaro.