1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Wasu matasa sun kai hari a ofishin 'yan sanda a Burkina Faso

Abdourahamane Hassane
January 19, 2019

Rahotanni daga Ouagadougou babban birnin Kasar Burkina Faso sun bayana cewar wasu mutane sun rasa rayukansu yayin da matasa suka far wa jami'an 'yan sanda bayan mutuwar wani matashi sakamakon harbin bindinga.

https://p.dw.com/p/3Bqid
Gewaltsame Proteste in Ouagadougou 28.10.2014
Hoto: AFP/Getty Images/Issouf Sanogo

 

Ma'aikatar tsaron kasar ta bayyana cewar tawagar wasu samari da yawansu ya kai 100 sun afka ofishin 'yan sanda na birnin Orodara da ke yammacin kasar da niyar daukar fansar wani matashi da jami'an tsaron suka harbe a ranar Juma'ar da ta gabata. Sakamakon binciken gaggawar da ma'aikatar tsaron kasar ta gudanar ya tabbatar da mutuwar biyar daga cikin matasan yayin da takwas suke cikin mawuyacin hali sakamakon muggan raunuka.