1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Za a fara binciken gawa a Burkina Faso

Abdul-raheem Hassan
July 16, 2019

Masu gabatar kara a Burkina Faso sun kaddamar da bincike mai tsanani kan mutuwar wasu mutane 11 a ofishin hukumar yaki da sha da fataucin kwaya a babban birnin kasar Ouagadougou.

https://p.dw.com/p/3M89P
Burkina Faso Ouagadougou Attacken in Innenstadt
Hoto: Getty Images/AFP/A. Ouoba

Mai gabatar da kara a kasar Maiza Sereme ta ce an bude babin binciken ne da neman kwararru su gudanar da sahihin bincike kan gawarwakin don tabbatar da silar mutuwarsu. An tsare mutanen ne bayan kamasu da zargin ta'ammali da muggan kwayoyin da ke sa maye.

Matsalar muggan kwayoyi na cikin manyan matsalolin kasar Burkina Faso, inda ake ganin rashin aiki ya sa kasar zama daya a cikin cibiyoyin kwayoyi a yammacin Afirka domin safararsu zuwa arewacin Mali da Libiya.