1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tsamin dangantakar Jamus da Chaina

Lateefa Mustapha Ja'afar
September 11, 2019

Rahotanni daga Chaina sun ce mahukuntan Beijing sun aika sammaci ga jakadan Jamus a kasar, abin da ke nuna yadda dangantaka ke shirin yin tsami tsakanin kasashen biyu.

https://p.dw.com/p/3PQxx
Joshua Wong vor der Bundespressekonferenz
Joshua Wong jagoran fafutukar tabbatar da dimukuradiyya a yankin Hong KongHoto: picture-alliance/dpa/W. Kumm

Mtakin Chainan dai na zuwa ne bayan da ministan harkokin kasashen ketare na Jamus din Heiko Maas ya gana da shugaban masu zanga-zanga a yankin Hong Kong Joshua Wong a farkon wannan makon. Jakadan Chainan a Jamus Wu Ken ya nunar da cewa Beijing ta bayyana rashin jin dadinta karara, kan ganawar tsakanin Maas da Wong yana mai cewa hakan ka iya janyo baraka a dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu. Dama dai sau da dama mahukuntan Chainan sun bukaci da a hana Wong takardar izinin shiga Jamus din wato visa, sai dai a wannan Larabar Joshua Wong da ke zaman jagoran fafutukar tabbatar da mulkin dimukuradiyya a Hong Kong din, ya halarci wani taron manema labarai a Berlin fadar gwamnatin Jamus, tare da yin kira ga mahukuntan na Berlin da su yi tir da yadda 'yan sanda ke murkushe masu zanga-zangar a yankin na Hong Kong da karfin tuwo.