1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ci gaba da fafata fada a Sudan ta Kudu

January 21, 2014

'Yan tawayen Sudan ta Kudu sun musanta ikirarin gwamnati na kwace garin Malakal

https://p.dw.com/p/1Au6y
Hoto: Samir Bol/AFP/Getty Images

'Yan tawayen Sudan ta Kudu sun musanta ikirarin gwamnatin kasar na sake kwato garin Malakal.

Garin na Malakal ya kasance karkashin gwamnati da 'yan tawaye cikin wata guda da aka shafe ana fafatawa tsakanin bangarorin. Rikicin ya samo asali lokacin da Shugaba Salva Kiir ya zargi tsohon mataimakinsa Riek Machar da yunkurin kifar da gwamnati.

Wani kiyasin Majalisar Dinkin Duniya ya nuna dubban mutane sun hallaka, yayin da wasu kimanin rabin miliyan suka tsere daga gidajensu sakamakon rikicin na Sudan ta Kudu. Masu shiga tsakani na fata bangarorin da ke rikici da juna za su amince da shirin tsagaita wuta.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Saleh Umar Saleh