1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana ci gaba da fuskantar tashin bama-bamai a Maiduguri

Al-Amin Suleiman Muhammad/LMJJune 2, 2015

A Najeriya ana ci gaba da fuskantar hare-hare a yankin arewa maso gabashin kasar da ke zaman tushen kungiyar Boko Haram da ke gwagwarmaya da makamai a kasar.

https://p.dw.com/p/1Fagr
Hare-haren Boko Haram a Najeriya
Hare-haren Boko Haram a NajeriyaHoto: picture-alliance/AP Photo/Jossy Ola

Wani bam da ya tashi a wata kasuwar dabbobi a Maiduguri fadar gwamnatin jihar Borno da ke yankin arewa maso gabashin Najeriya ya hallaka mutane da dama yayin da wasu kuma suka jikata. Shaidun gani da ido sun bayyana cewa da misalin karfe daya na rana ne suka ji kara mai karfi nan take kuma mutane suka ranta a na kare. Ya zuwa yanzu dai babu cikakken bayani kan yadda al'amarin ya faru kana babu masananiya kan adadin wadanda harin bam ya rutsa da su. Wani kwamandan matasan nan da aka fi sani da Civilian JTF ya tabbatar wa da wakilinmu na Gombe Al-Amin Suleiman Muhammad da tashin bam din.