Ci gaban rikicin Irak
February 28, 2006Tashe tashen hankulla babu ƙaƙƙabtawa, na ci gaba da hadasa asara rayuka a ƙasar Iraki.
A ranar yau talata, wasu yan ƙunar baƙin wake sun kai tagwayen hare hare a birnin Bagadaza.
Mutane kimanin 30 sun rasa rayuka, sannan da dama, sun ji mumuman raunuka.
Bugu da ƙari wani hari makamancin wannan ,ya wakana a tsakiyar kasuwar garin Karrada, wanda shima ya jawo assara rayuka 4.
Daga barkewar rikicin addinin ranar laraba da ta wuce, zuwa yanzu, mutane kussan 400 su ka rasa rayuka.
A ɓangasen siyasa kuma, wani rikici ya kunnu tsakanin Shugaban ƙasa Jallal Talabani ,da Praminista Ibrahim Jafari.
Shugaban ƙasar, ya zargi Praminista, da kai ziyara a ƙasar Turquia, ba tare da ya sanar da shi ba.
Ibrahim Aljaafari, ya tantana da takwaran sa, Tayib Erdowan, a game da tashe tashen hankulla da ke wakana a ƙasar Irak, tsakanin yan sunni day an shi`a.
Pramistan Turquia, ya gayyaci ƙasashen yanki baki ɗaya, da su bada haɗin kai, a samo ruwan kashe wannan wuta, wace idan ta ci gaba, za ta yaɗuwa a dukkan ƙasashen yankin.