1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Senegal cin galabar COVID-19

May 12, 2020

Hukumomi a kasar Senegal sun bayar da sanarwar bude masallatai da mujami'u a woni kokarin farfado da harkokin walalar jama'a bayan barkewar annobar coronavirus

https://p.dw.com/p/3c8aG
Senegal Dakar | Pflegepersonal | Pikine Hospital
Hoto: Getty Images/AFP/J. Wessels

Shugaba kasar ta Senegal Macky Sall shi ne ya bayar da wannan sanarwar tare da sassauta dokar hana zirga-zirga da aka kakaba domin yaki da annobar Corona.

Kasar ta Senegal na kan gaba cikin kasashen duniya da suka ci karfin annobar ta coronavirus da ta kama mutane 1886 a kasar, inda tuni 715 suka murmure daga cutar, kana mutune 19 ne  suka mutu bayan kamuwa da cutar.

A wani yunkuri na baya-bayan nan, kasar ta fara gwajin na'urorin gwajin cutar cikin mintoci 10, kuma masu saukin kudi da mutum zai iya gwada kansa daga gida. Haka zalika gwamnatin Senegal ta amince a gwada maganin gargajiya da aka samu a kasar Madagaska.