1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Cutar Corona na kara kamari a Saudiyya

Gazali Abdou TasawaAugust 19, 2015

Hukumomin kiwon lafiya na kasar ta Saudiyya sun ce an samu sabbin kamuwa da cutar ta matsalar nunfashi guda 50 a cikin wannan wata na Agusta kadai.

https://p.dw.com/p/1GHXW
Südkorea MERS
Hoto: Reuters/Kim Hong-Ji

Hukumomin kiwon lafiya a kasar Saudiyya sun bada sanarwar samu karin wasu mutane 50 da suka kamu da cutar matsalar nunfashi ta Corona a kasar a cikin wannan wata na Ogusta kadai. Hukumomin kasar ta Saudiyya sun ce a ranar Larabar jiya kadai an samu mutane 10 da suka kamu da wannan cuta. Yaduwar wannan cuta ta Corona dai ya zo ne a daidai lokacin da kasar ta Saudiyya ke shirin soma karbar bakunci miliyoyin maniyata da za su je domin sabke faralin shekarar bana.

A shekara ta 2012 ne dai wannan cutar matsalar nunfashi mai saurin kisa ta Corona ta bayyana a kasar ta Saudiyya inda ta yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama. Mutane kimanin 800 ne wannan cuta ta hallaka a duniya baki daya tun bayan bullowarta ta farko a shekara ta 2002.