1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Cutar Ebola ta hallaka mutane a Saliyo

May 26, 2014

Rahotannin daga kasar Saliyo na cewar mutane hudu sun rasu sakamakon kamuwa da kwayar cutar nan ta Ebola mai saurin hallaka mutane.

https://p.dw.com/p/1C75H
Ebola-Virus in Guinea
Hoto: Seyllou/AFP/Getty Images

Jami'an kiwon lafiya a kasar yanzu haka na cigaba da gudanar da bincike kan yankin da aka samu bullar cutar da ma dai inda mutanen suka rasu ko ya Allah za a samu karin wanda ke dauke da kwayar cutar don killace su kafin su kai ga yada ta.

A makonnin bayan ne dai aka samu bullar wannan cutar ta Ebola a yankin yammancin Afirka inda aka samu rasuwar mutane da dama a Gini Konakry, al'amarin da ya sanya kasar rufe iyakokinta da makotanta don gudun bazuwar kwayar cutar.

Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Mohammad Nasiru Awal