Cutar sankarau na kashe rayuka a Najeriya
March 28, 2017Talla
Cutar Dan sankarau na kokarin mamaye yankin arewa maso yammacin Najeriya Inda ake kara samun yawaitar mutane masu mutuwa kusan kowace rana a Jihohin Sokoto da Kebbi da Zamfara. Mafi yawancin alkalumman gwamnati na bayyana yawan wadanda suka mutu a asibiti a yayin da wasu ke mutuwa a gidajensu saboda rashin abin hannu da za su dauki dawainiyar kansu a asibiti.Yanzu haka dai hukumomin lafiya na daukar matakai na shawo kan matsalar ta hanyar riga kafi da ba da magani da kuma yekuwar wayar da kai a kan kaucewa kwanciya a cikin dakuna saboda tsananin zafi.
A shekarun baya ma daI haka aka yi ta fama da irin wannan annoba ta cutar dan sankarau a cikin jihohin na arewacin Najeriya.