1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dakarun Iraki na samun nasara kan IS

Lateefa Mustapha Ja'afarAugust 24, 2016

Dakarun Iraki sun samu nasarar kwace iko da garin Al-Qayyarah daga hannun kungiyar IS. Garin na Al-Qayyarah dai na kusa da birnin Mosul da 'yan kungiyar ta IS suke da karfi.

https://p.dw.com/p/1Jp9H
Dakarun Iraki sun samu narar kwace garin Al-Qayyarah
Dakarun Iraki sun samu narar kwace garin Al-QayyarahHoto: Reuters

Kwamandan dakarun na Iraki da ke samun goyon bayan sojojin Amirka a yankin da suke da IS din, Nejm al-Jabouri ya shaidawa kamfanin dillancin labaran Jamus na DPA cewa tuni ma sojojinsa suka kwace iko da matatar mai da ke garin. Sai dai al-Jabouri ya nunar da cewa wasu jerin hare-haren kunar bakin wake da kungiyra ta IS ta kai da motoci ya dakile yunkurin da dakarunsa ke yi na sake kutsawa wasu yankunan garin na Al-Qayyarah da ke da nisan kilomita 60 da kudancin birnin na Mosul.