1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Daukar tsauraran matakan tsaro a Sahel

November 14, 2013

Ministocin yankin Sahel da Magreb sun hallara a birnin Rabat din kasar Moroko, domin tattauna hanyoyin bunkasa tsaro da kare kan iyakokin kasashen daga 'yan tawaye

https://p.dw.com/p/1AHzW
FILE - In this March 18, 2004, file photo Malian soldiers from the 512th Motorised Infantry company complete their training by U.S. Special Forces, top, in the desert near Timbuktu in Mali as part of the U.S. Pan-Sahel Initiative to secure the Sahel region from being used by terrorists. On Sunday April 1 2011, nomadic Tuaregs who descended from the people who first created Timbuktu in the 11th century and seized it from invaders in 1434, attacked the city in their fight to create a homeland for the Sahara's blue-turbaned nomads. Their assault deepens a political crisis sparked March 21 when mutinous soldiers seized power in the capital. The Tuaregs have rebelled before, but never have they succeeded in taking Timbuktu or the major northern centers of Kidal and Gao, which fell Friday and Saturday as demoralized government troops retreated. (Foto:Ben Curtis, File/AP/dapd)
Hoto: dapd

Ministocin harkokin waje na kasashen da ke yankin Sahel da Magreb, suna taro a birnin Rabat din kasar Moroko domin tattauna matakan inganta tsaro kan iyakokin su tare da kalubalantar masu tsattsauran ra'ayi da ke barazana a yankin. Anasaran halartar manyan jami'an Amurka da Birtaniya da Faransa. Taron dai a cewar ministan sadarwan Moroko Mustafa Khalfi, na da nufin samar da hadin gwiwa tsakanin kasashen yankin, tare da sanya fifiko kan kasashen Mali da Libiya. Har yanzu dai kasar Mali na fuskantar hare hare na mayakan tawaye, watanni 10 bayan da dakarun Faransa suka kai somame a kan kungiyoyin 'yan tawaye da ake alakantawa da ta Al-Qaeda, wadanda suka samu gindin zama a yankin arewacin kasar, inda aka yi wa wasu 'yan jaridar Faransa kisan gilla a farkon watan Nuwamba. Kwararru kan tsaro dai sun yi gargadin cewar, a yanzu haka irin wadannan kungiyoyin tarzoma na samun gindin zama a cikin sahara da ke kudancin Libiya.

Mawallafiya: Zainab Mohammed Abubakar
Edita : Pinado Abdu-Waba