1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kokarin dakile ayyukan tarzoma a Chadi

Lateefa Mustapha Ja'afarJuly 31, 2015

Gwamnatin kasar Chadi ta sake dawo da yanke hukuncin kisa ga masu manyan laifuka watanni shida bayan soke hukuncin a kasar.

https://p.dw.com/p/1G7yP
Shugaban kasar Chadi Idriss Deby
Shugaban kasar Chadi Idriss DebyHoto: Thierry Charlier/AFP/Getty Images

Hakan dai ya biyo bayan amincewa da 'yan majalisun dokokin kasar suka yi da wata sababbin tsauraran dokoki na yaki da ta'addanci sakamakon hare-haren da kasar ke fuskanta daga kungiyar Boko Haram da ta addabi Najeriya da makwabtanta. Tun dai bayan da aka fuskanci munanan tagwayen hare-haren kunar bakin wake a N'Djamena babban birnin kasar, mahukuntan na Chadi suka sake daukar kwararan matakan tsaro, da suka hadar da soke amfani da Hijabi da kuma barace-barace. Sai dai 'yan adawa da kuma kungiyoyin masu fafutuka na nuna fargabarsu ga sababbin dokokin da gwamnatin ta kafa da suke cewa za su iya take hakkin dan Adam a kasar. A hannu guda kuma baya ga hukuncin kisa ga wadanda suka aikata manyan laifukan ta'addanci majalisar ta mayar da hukuncin masu kananan laifukan ta'addancin daga shekaru 20 zuwa daurin rai-da-rai.