1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

De Maiziere na ziyara a yankin Magreb

Kamaluddeen SaniFebruary 29, 2016

Ministan harkokin cikin gidan tarayyar Jamus na fara ziyarar ne da kasar Morocco domin neman hadin kan kasashen kan batun 'yan gudun hijira da ake shirin mayarwa gida

https://p.dw.com/p/1I4FO
Deutschland Innenminister Thomas de Maizière
Hoto: picture-alliance/dpa/W. Kumm

Ziyarar dai ta ministan harkokin cikin gidan Jamus din dai na zama wani yunkuri baya-bayan nan da hukumin Jamus su ke kan takaita kwarar 'yan gudun hijira zuwa kasar.

Ita dai wannan tattaunawar tsakanin kasashen biyu na zama yunkurin farko a cikin ziyarar kwanaki uku da Minstan yake a yankin Magrib da suka hada da kasashen Aljeriya da Tunisiya gami da ita kanta Moroccon don tattauna matsalar 'yan gudun hijira da kuma samun mafuta a tsakanin kasashen.

Thomas de Maiziere ya ce " a 'yan kwanakin nan masu neman mafaka daga Morocco da Algeriya da Tunisiya sun shigo Jamus da yawan su, wadanda ba su da damar zama a nan, a don haka akwai bukatarmu tattaunawa da gwamnatocin Morocco da Aljeriya da Tunisiya kan yadda za mu maido da su cikin nutsuwa, a shirye muke kuma mu tallafa wajen mai da su kasashen su na asali".