1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dubban 'yan sanda sun yi zanga-zanga a Tunisiya

Salissou BoukariJanuary 25, 2016

A kalla 'yan sanda 3,000 ne suka yi jerin gwano a wannan Litinin din a birnin Tunis na kasar Tunisiya ya zuwa fadar shugaban kasar ta Chartage domin neman karin albashi.

https://p.dw.com/p/1HjXu
Hoto: picture-alliance/dpa

'Yan sandan na rera cewa albashinsu dai bai taka kara ya karya ba, sannan kuma sune ke sadaukar da rayukansu wajan kariyar kasa, don haka suna bukatar abun da suke gani halaliya ne a gare su. Jami'an tsaron kasar Tunisiya dai na taka rawar gani wajan yaki da 'yan kungiyar IS inda su ne kuma kan gaba wajan fuskantar hare-haren 'yan kungiyar, inda a bara ma aka kaiwa jami'an da ke tsaron shugaban kasar hari tare da hallaka da dama daga cikin su.