Duniya za ta taimaka wa Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya
November 26, 2013Faransa ta ce a shirye ta ke ta aike da ƙarin sojoji 800 a Jamhuriyar ta Afirka ta Tsakiya da ke fuskantar wani mummunar halin na tashin hankali. Wanda ƙasashen duniya suka bayyana fargabnsu a kan ta'addin da ake tafawa na aikata kisan gila da fyaɗe akan al'ummar ƙasar. Mataimakin sakataran MDD Jan Eliasson ya ce tilas ne a ɗauki matakai na gaggawa domin magance abubuwan na asha da ke faruwa a ƙasar.
A wani zaman da kwamitin sulhu na MDD ya yi a jiya, Faransa ta ce za ta ajiye wani daftari ƙudiri a gaban majalisar na sake dawo da doka a ƙasar da ta faɗa cikin ruɗani da rashin tabbas.Tun bayan juyin mulkin da ƙungiyar 'yan tawaye ta SELEKA a ƙarƙashin jagorancin , Michel Djotodia ta yi wa Francois Bozize a cikin wata Maris da ya gabata.
Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Usman Shehu Usman.