1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ebola ta kawo fatara a Saliyio

Abdourahamane HassaneNovember 27, 2014

Hukumar abinci ta Majalisar Ɗinkin Duniya FAO ta ce a yankunan da cutar Ebola ta ɓulla a ƙasar ana fama da matsala ta ƙaranci abinci,

https://p.dw.com/p/1DvXS
Ebola Conakry European Union Helfer
Hoto: European Union/Kenzo Tribouillard

A wani binciken da ta gudanar hukumar ta ce a cikin kishi ɗari, kishi 70 na jama'ar da aka yi wa tambayoyin sun ce sau ɗaya suke cikin abinci a yini.

Darakatan hukumar da ke ƙokarin shawo kan cutar ta Ebola Martin Vincent,wanda hukumarsa ta gudanar da bincike na haɗin gwiwa tare da hukomin PAM da na FAO.Ya ce fatara da manoma ke fama da ita, ta janyo musu cikas wajen yin aikin noman, don haka dole sai an taimaka musu domin su sake farfaɗowa.