Jakadun EU sun amince da karin takunkumin Rasha
June 17, 2015Talla
Kasashe da ke zama mambobi a kungiyar EU a ranar Laraban nan sun amince su kara wa'adin lokacin da suka tsara na sanya takunkumi kan kasar Rasha saboda kutsen da take yi a kasar Ukraine.
Ya zuwa yanzu dai an kara wata shida na wannan takunkumi, kenan zai kare a karshen watan Janairu na shekarar 2016, kamar yadda majiyar kungiyar ta nunar.
A cewar majiyar, jakadu daga kasashe mambobin wannan kungiya 28 sun cimma matsaya kan shirin kara wa'adin takunkumin tun daga watan Yuli sannan za a tura wa taron ministoci na kungiyar ta EU ranar Litinin dan su samu su rattaba hannu.