1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

EU ta cimma matsaya kan makomar Birtaniya

Abdul-raheem Hassan
December 15, 2017

Shugabannin kungiyar Tarayyar Turai sun cimma matsaya a hukumance na bude sabon babin tattaunawa kan makomar dangantaka da huldar kasuwanci da Birtaniya.

https://p.dw.com/p/2pRPA
Belgien May und Juncker in Brüssel
Hoto: Reuters/Y. Herman

Da yake bayani a birnin Brussels na kasar Beljiyam, shugaban hukumar Tarayyar Turai Jean-Claude Junker ya jinjinawa firamistar Birtaniya Theresa May a kan yunkuri na cimma burinta. Amma ya yi gargadin cewa tattaunawa da za a shiga nan gaba na iya daukar zafi fiye da ta farko.

A daya bangaren bangaren Theresa May da take martani a shafinta na Twitter bayan cimma matsayar ci gaba da tattaunawar, ta ce "Yau an cimma gagarumar nasarar kama hanyar kammala ficewa daga EU a cikin ruwan sanyi, tare da duba makomar Birtaniya bayan ficewa daga kungiyar Tarayyar Turai."

A watan Yunin shekara ta 2016 ne Birtaniya ta kada kuri'ar raba gardama na neman balewa daga kungiyar EU, sai dai ana sa ran ballewar za ta kai watan karshen watan Maris na shekarar 2019.