1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

EU ta tallafa wa Italiya saboda girgizar kasa

Yusuf Bala Nayaya
August 30, 2017

Kwamitin kasafi na majalisar ya amince da bada wannan kudi daga asusun hadaka na Kungiyar EU, wato daga kudaden da ake amfani da su wajen tallafawa mambobi.

https://p.dw.com/p/2j7Cp
Italien Erdbeben
Hoto: pictureialliance/AP Photo/Sky Italia

Majalisar Kungiyar Tarayyar Turai a wannan rana ta Laraba ta amince da bada kudi tsaba Euro miliyan dubu da dari biyu don tallafa wa al'umma da suka fiskanci bala'in girgizar kasa a Italiya a shekarar bara da wannan shekara.

Kwamitin kasafi na majalisar ya amince da bada wannan kudi daga asusun hadaka na Kungiyar EU, wato daga kudaden da ake amfani da su wajen tallafawa mambobi na kungiyar da suka fiskanci wani bala'i.

Girgizar kasa da aka rika samu daga watan Agusta 2016 zuwa Janairu 2017 ta shafi al'umma da dama a Tsakiyar Italiya. Fiye da mutane 330 suka rasu yayin da sama da 30,000 suka kauracewa muhallansu, baya ga wadanda harkokin kasuwacinsu ya gurgunce.