1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

EU ta yi kiran da a rusa kungiyar M23

November 1, 2013

Kungiyar tarayyar Turai ta EU ta yi kira ga mahukuntan Jamhuriyar Dimokradiyyar Kongo da su rusa kungiyar 'yan tawayen nan ta M23 da ke dauke da makamai.

https://p.dw.com/p/1AADl
'Yan tawayen M23 na Jamhuriyar Dimokradiyar KongoHoto: Carl de Souza/AFP/Getty Images

Mai magana da yawun ofishin harkokin wajen na kungiyar ta EU Sebastien Brabant ne ya yi wannan kiran, inda ya ce ya kyautu a gaggauta kammala tattaunawar da ake ta kokarin wanzar da zaman lafiya a kasar wadda ke gudana a kasar Uganda, da ma dai kawo karshen kungiyar ta M23.

Baya ga wannan, Mr. Brabant ya ce akwai bukatar da ke akwai wajen ganin an dakile aiyyukan dukannin wata haramtaciyyar kungiya a kasar da ke dauke da makamai.

To sai dai a hannu guda Brabant din ya ce gwamnatin kasar ta guji daukar duk wani mataki na ramuwar gayya ko kuma cin zarafin fararen hula.

Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Umaru Aliyu