1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Turkiya da Siriya za su samu tallafin EU

February 9, 2023

Shugabannin kasashen Tarayyar Turai 27 sun dauki alkawarin bai wa Turkiya taimako iya karfinsu don rage radadin bala'in girgizar kasa da ta auku a kasar da Siriya.

https://p.dw.com/p/4NI5O
Syrer in Deutschland zeigen Solidarität mit den Erdbebenopfern in Syrien und der Türkei
Hoto: Mohammed Magdy/DW

Shugabannnin Tarayyar Turai  27 suka rattaba hannu kan takardar wace suka aika wa shugaban kasar Turkiya Recep Tayyip Erdogan, inda suka nuna masa matukar goyon bayansu a dai-dai lokacin da kasarsa ta shiga wani rikicin ba zata. Shugabannin na EU a taronsu na wannan Alhamis a birnin Brussel, sun kuma yi tsit na miniti guda don tunawa da 'yan Turkiya da da Siriya da suka mutu a girgizar kasar. Shugabannin sun ce taimakonsu ga 'yan Turkiya da Siriya, sai iya inda karfinsu ya tsaya.  A daya bangaren taron na Brussel sun gayyaci shugaban kasar Ukraine a taron, wanda ya jaddada bukatarsa ta neman lallai sai kasashen Yamma su gaggauat aika wa kasarsa makamai yayinda yakinsu da Rasha ke kara daukar lokaci.