1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Fada ya barke a Bangui

April 14, 2013

An yi wani kazamin fada tsakanin magoya bayan hambararen shugaban Afirka ta Tsakiya Francois Bozize da sojojin 'yan tawayen Seleka a tsakiyar birnin Bangui inda mutane 7 suka kwanta dama.

https://p.dw.com/p/18FjY
Hoto: AFP/Getty Images

 An yi wani kazamin fada tsakanin magoya bayan tsohon hambararen shugaban kasar Afirka ta Tsakiya da kuma a dai share daya 'yan tawayen da suka kame iko daga kasar.

Fadan ya barke ne a yayin da sojojin 'yan tawayen ke sintiri a tsakiyar birnin na Bangui a unguwar Boy Rabe cibiyar magoya bayan hambararen shugaban inji Janar Nousa Dhaffane kakakin rundunar 'yan tawayen.

A na shi bangare babban jami'in asibitin birnin na Bangui Roman Guetiza ya ce an kai masu gawarwakin mutane kimanin guda bakwai, yayinda aka biya da wasu 9 da suka samu raunika.

A ran Asabar ne komitin koli na 'yan tawayen ya nada jagoran kungiyar ta 'yan tawayen Seleka Michel Djotodia a matsayin sabon shugaban kasar.

Mawallafi: Issoufou mamane

Edita ; Umaru Aliyu