Fada ya barke a Bangui
April 14, 2013An yi wani kazamin fada tsakanin magoya bayan tsohon hambararen shugaban kasar Afirka ta Tsakiya da kuma a dai share daya 'yan tawayen da suka kame iko daga kasar.
Fadan ya barke ne a yayin da sojojin 'yan tawayen ke sintiri a tsakiyar birnin na Bangui a unguwar Boy Rabe cibiyar magoya bayan hambararen shugaban inji Janar Nousa Dhaffane kakakin rundunar 'yan tawayen.
A na shi bangare babban jami'in asibitin birnin na Bangui Roman Guetiza ya ce an kai masu gawarwakin mutane kimanin guda bakwai, yayinda aka biya da wasu 9 da suka samu raunika.
A ran Asabar ne komitin koli na 'yan tawayen ya nada jagoran kungiyar ta 'yan tawayen Seleka Michel Djotodia a matsayin sabon shugaban kasar.
Mawallafi: Issoufou mamane
Edita ; Umaru Aliyu