1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Fafaroma ya yi kashedi ga bayyana kalaman wariya

Abdourahamane Hassane
November 15, 2019

Fafaroma Francis ya yi kiran da a yi hattara a game da irin kalaman da 'yan siyasa ke yadawa a yanzu wanda ya ce suna yi masa tuni da irin na 'yan mulkin Nazi.

https://p.dw.com/p/3T8Fe
Papst Franziskus
Hoto: Reuters/R. Casilli

Fafaroma Francis ya ce kalaman na 'yan siyasa sun yi kama da irn jawabin da Hitler ya rika yi na nuna kyama ga Yahudawa da kuma 'yan luwadi da madigo. Fafaroma wanda ya bayyana haka a loacin wata ganawa da jami'an wata kungiyar ta kare hakin bil Adama na kasa da kasa ya ce ya zama waji a rika saka ido ga abin da ka iya zama fitina ga duniya. Fafaroma Francis ya yi kashedi ga irin tsongoma da ake kokarin sake dawo da ita a kan Yahudawa.