1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Falasɗinawa na yin zaɓukan magadan gari

October 20, 2012

Falasdinawa sun fara gudanar da zabuka na magadan gari a gabar yamma ta kogin Jordan inda ake sa ran kimanin mutane rabin miliyan za su kaɗa kuri'unsu.

https://p.dw.com/p/16ToB
An international observer monitors as a Palestinian security man casts his vote for the parliamentary elections in the West Bank city of Nablus, Sunday, Jan. 22, 2006. Palestinian security forces cast ballots for parliamentary candidates Sunday in the official second day of this week's Palestinian elections - an advance vote that reflected the fragile security situation in the West Bank and Gaza Strip. (AP Photo/Emilio Morenatti)
Hoto: AP

Da misalin ƙarfe biyar na safiyar yau ne dai agogon GMT aka buɗe rumfunan zaɓe a yanki kuma ana sa ran kammala shi da misalin ƙarfe biyar na yamma agogon na GMT kana sakamakon farko na zaɓen zai bayyana da sanyin safiyar gobe lahadi idan Allah ya kaimu.

Kimanin 'yan takara dubu huɗu da dari bakwai wanda kashi ashrin da biyar daga cikinsu mata ne za su fafata a zaben wanda shi ne irinsa na farko cikin shekaru shiddan da su ka gabata.

Mawallafi : Ahmed Salisu
Edita : Zainab Mohammed Abubakar