1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron zai maida hankali a kan yarjejeniyar MINSK

Abdourahamane HassaneJune 23, 2015

Ministocin harkokin waje na ƙasashen Rasha da Ukraine da Faransa da kuma Jamus na tattaunwa a birin Paris na Faransa a kan rikicin na Ukraine.

https://p.dw.com/p/1FmEe
Außenministertreffen zur Ukraine-Krise
Hoto: Reuters

Ministocin na waiwaye adon tafiya ne a game da inda aka kwana dangane da aiwatar da yarjejeniyar MINSK a Ukraine.Wannan saduwa dai na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan da Ƙungiyar Tarrayar Turai,ta amince da wani ƙudirin tsawaita takunkumin karya tattalin arziki ga Rasha saboda rawar da take takawa a yaƙin da ake yi a gabashin Ukraine.

An dai ci gaba da gwabza yaƙi tsakanin dakarun gwamatin da na 'yan aware a gabashin ƙasar duk da yarjejeniyar tsagaita buɗe wutar da aka cimma a watanni huɗun da suka gabata.