Faransa ta halaka wasu 'yan tawaye
February 14, 2018Talla
Wani harin da sojojin Faransa suka kaddamar ta sama a arewa maso gabashin kasar Mali, ya halaka wasu masu gwagwarmaya da makamai su 10 a kan iyakar kasar da kasar Aljeriya. Wata majiyar jami'an tsaro ta ce harin na yau Laraba, ya kuma lalata wasu kayayyakin yakin 'yan bindigar ciki har da motocinsu.
Harin dai na daga cikin ayyuka ne na sintirin Barkhane da ke aiki a kasashen Mali da Moritaniya da Nijar da Chadi da kuma Burkina Faso. Dakarun kasar Faransar dai sun dauki kwanaki suna aikin tabbatar da tsaro a arewa maso gabashin kasar ta Mali.
Wasu rahotanni kuma daga kasar Burkina Faso, sun tabbatar da kashe wani jami'in dan sanda tare da jikkata wasu a wani harin na 'yan bindiga a garin Fada N'Gourma.