1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Faransa ta sanar da jadawalin janye sojojinta daga Mali

March 7, 2013

Shugaban Faransa Francois Hollande ya ce a ranar daya ga watan Afrilu sojojin kasarsa za su fara janyewa daga Mali. A cikin

https://p.dw.com/p/17saV
Hoto: Getty Images

A cikin jawabin  da ya yi yayin ziyarsara a birnin Warsaw na kasar Poland, Hollande yac e sojojin za su kwashe watan Maris suna gudanar da aiki a kasar ta yammacin Afirka. A wancan wata na Fabarairu ministan harkokin wajen kasar ta Faransa, Laurent Fabius ya ce daga watan Maris ne sojojin za su fara ficewa daga  Mali. Shugaba Hollande ya kira aikin  da sojojin  ke yi a Mali tamkar wani muhhimmin mataki wajen yaki da taaddanci. Su dai yan kishin Islamar an samu nasarsar fatattakarsu daga  manyan biranen dake Arewacin kasar, to amma su kan shiga yin aratabun da ba a rasa ba a yankin Ifogha. Yayin ziyara tasa a birnin Warsaw, Hollande  ya kuma tattauna tare da shugabar gwamnatim Jamus, Angela Merkel da shugabannin kasashen Poland da Hungary da Cek da Slovakia inda suka mai da hankali ga bukatar karfafa yin hadin-gwiwa a fannin tsaro.

Mawallafiya: Halima Balaraba Abbas
Edita: Zainab Mohammed Abubakar