1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Faransa ta yaba da zaɓen Mali

July 29, 2013

Faransa ta kira zaɓen Mali "babbar nasara" zaɓen da ta gudanar a karon farko tun bayan juyin mulki da rikicin da Faransar ta taimaka wajen daƙilewa.

https://p.dw.com/p/19GdL
French President Francois Hollande replies to questions after his speech at the Elysee Palace in Paris May 16, 2013. REUTERS/Benoit Tessier (FRANCE - Tags: POLITICS)
Francois HollandeHoto: Reuters

Firaministan Faransa Jean-Marc Ayrault ya jinjinawa ƙasar Mali da ta iya ta gudanar da abin da ya kira zaɓe mai nasara musamman ma ga Faransa wadda ta tura dakarunta ƙasar suka tasa ƙeyar ƙungiyoyin masu kaifin kishin addini.

Lokacin wata ziyara da ya kai ƙasar Malaysia Firaminista Ayrault ya aikawa mahukuntar ƙasar gaisuwar taya murnarsa, ya kuma ce nasarar zaɓen ya ɗaga ƙimar Faransa a idon duniya, musamman ga waɗanda suka ƙyamace ta saboda rawar da taka a lokacin da ƙasar ta Malin ta shiga mawuyacin hali sakamakon juyin mulki da rikicin da ya biyo baya.

Kawo yanzu dai ba a fitar da sakamakon zaɓen a hukumance ba, to sai dai shugaban ƙasar Faransa Francois Hollande ya ce yana farin cikin ganin an gudanar da zaɓen ba tare da wata gagarumar matsala ko tashe-tashen hankula ba.

Mawallafiya: Pinaɗo Abdu Waba
Edita:            Yahouza Sadissou Madobi