1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gwamnatin Faransa ta dauki matakin faranta wa 'yan sanda

Zulaiha Abubakar MNA
December 19, 2018

Shugaba Emmanuel Macron na Faransa ya baiyana shirin gwamnati na biyan jami'an 'yan sandan da ke aiki a yankunan da suka fuskanci tarzoma kudin da yawansu ya kai Euro 300 kowane mutum daya.

https://p.dw.com/p/3AMJ1
Emmanuel Macron Rede an die Nation
Hoto: Reuters/L. Marin

Wannan na zuwa ne kwana guda bayan da wasu kungiyoyin 'yan sandan kasar suka sanar da shirinsu na janyewa daga bakin aiki don gudanar da zanga-zanga kan wasu bukatu da suka hada da karancin ma'aikata da batun kasafin kudi.

Har ya zuwa wannan lokaci babu tabbacin amincewa da wannan tayi daga bangaren 'yan sandan kasar ta Faransa. Koda yake za a gudanar da wani taro tsakanin ministan harkokin cikin gida da kuma wakilan kungiyar 'yan sanda a wannan Larabar bayan da kungiyar 'yan sandan ta rabawa manema labarai wata sanarwa inda suka baiyana cewar sun fi karfin a siyo su da kudi.