1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Fargabar yakin basasa tsakanin Kurdawa

August 16, 2017

Turkiya ta yi gargadin barkewar yakin basasa.Idan Kurdawa suka ci gaba da yunkurin ballewa daga Bagadaza

https://p.dw.com/p/2iLTt
Irak Kurdinnen mit Flagge Kurdistans
Hoto: Getty Images/AFP/S. Hamed

Ministan harkokin wajen Turkya Mevlut Cavusolgu ya yi kashedin barkewar yakin basasa idan gwamnatin yankin Kurdawa a arewacin Iraqi ya ci gaba da shirin gudanar da kuri'ar raba gardama na ballewa daga Bagadaza domin ayyana yancin cin gashin kai.

Turkiyar wadda ke da Kurdawa yan tsiraru ta na kakkausar adawa da kuri'ar raba gardamar.

Shi ma dai Firaministan Iraki Haider al Abadi yana adawa da matakin kuma yanzu haka yana tattaunawa da bangarori daban daban domin tabbatar da cigaban kasar a matsayin kasa daya dunkulalliya.