1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Farmaki kan 'yan Boko Haram a Sambisa

Ahmed SalisuFebruary 19, 2015

Sojojin Najieriya sun ce sun hallaka mayakan Boko Haram da yawa a farmakin da suka kai ta sama a dajin Sambisa da garin Gwoza a jihar Borno da ke arewa maso gabashin kasar.

https://p.dw.com/p/1Eep3
Nigeria Kampf gegen Boko Haram Islamisten
Hoto: picture-alliance/AP

Mai magana da yuwun rundunar sojin Manjo Janar Chris Olukolade ya ce hare-haren da suka kai ta sama sun yi nasara matuka musamman ma a dajin na Sambisa idan kungiyar ke da sansanoni.

A 'yan kwanakin da suka gabata sojin na Najeriya sun ce sun hallaka 'yan kungiyar kimanin 300 a samamen da suka kai garururwa da dama inda suka karbe iko da su daidai lokacin da takwarorinsu da ke yakar kungiyar a Chadi da Kamaru da Nijar su ma suke bada labarin samun nasara a yakin da aka daura da Boko Haram din.