1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Firiministan Slobania ya gargadi kungiyar EU

Kamaluddeen SaniOctober 25, 2015

Miro Cerar yayi gargadin cewar kungiyar tarayyar Turai na iya daddarewa muddin dai aka kasa shawo kan matsalar 'yan kugun hijirar da ke cibaga da tsallakowa na hiyar nan da makonni masu zuwa.

https://p.dw.com/p/1Gu2c
Miro Cerar
Hoto: Jure Makovec/AFP/Getty Images

Miro yace muddin kungiyar ba dauki wasu matakan gaggawa ba nan da wasu makonni dake tafe to a gaskiya kungiyar EU na iya kama hanyar wargajewa.

Kasar Slobania dai dake kasancewar karamar kasa mai yawan mutane miliyan biyu na fuskantar matsalar tsallakowar 'yan gudun hijira har sama da dubu 60.