Gano kasusuwa masu tsayin gaske a Niger
August 20, 2014
Maitre Soule Garba Masanin wanda ke nazari a kan alakar Misrawa da Hausawa ya gano wadannan kasusuwa ne a wani gari mai suna Dankurhwa da ke da nisan kimanin kilomita biyu da dalar dutse a kauyen Danbaki na cikin jihar Damagaram ta jamhuriyar Nijar.
Tun da farko dai Soule Garba wanda kwararre ne a fannin ilimin binciken tarihin Misrawan musamman dangane da abun da ya shafi haruffan rubuce-rubucensu, ya yi nasarar warware ma'anar haruffan rubutun Misrawa cikin harshen Hausa, abin da kuma ya ba shi kwarin gwiwar cewa Misrawan da na zamanin fira'auna na magana a cikin harshen Hausa. Hakan kuma ya bashi damar karanto wasu labarai da ke kunshe a cikin littafan nasu da kuma abun mamakin da ke cikin kalmomin Hausa dama sunayen garuruwan duniyar Hausa a yau.
Maitre Sule Garba ta wanann haya ce ma dai ya yi nasarar gano dalar dutsen garin Danbaki a garin Tirminin jahar Zinder a yau sama da shekaru biyu.Dalar dutsen da ya bayyana ta a matsayin dalar dutse na farko da aka yi a duniya tun kafin ruwan dufana, da tuni ta gabaci gine-ginen pyramide din da ake gani a yau a kasar Masar. A ci gaban binciken neman tabbatar da sahihancin wannan labarin nasa na nuna kasar Hausa ita ce tushen duniya, Maitre Sule ya kuma gano wadannan manyan kasusuwan da tsawonsu ya wuce mizani a kauyen Dankurhwa.
Yanzu haka dai tarin kasusuwan irin wadannan dogwayen gawarwaki ne ke akwai barkatai a cikin kushewun kwarin garin na Dankurhwa a ko wane kewaye da kananan duwatsu, kuma wani dattijo dan kimanin shekaru dari da ke rayuwa a wanann kauye na ya ce kakanninsu ma anan su ka iske wadannan kasusuwa masu ban mamaki.
Mawallafi: Gazali Abdou daga Yamai
Edita:Yusuf Bala