Garkuwa da wasu 'yan Faransa a Kamaru
February 19, 2013Talla
Rahotanni sun ce a yankin arewacin kamaru, an yi garkuwa da wani Iyalin Faransawa bakwai a ciki har da ƙananan yara guda huɗu, inda kamfanin dillancin labarun Associated Press ya rawaito cewa wasu jami'ai na zargin ƙungiyar Boko Haram da hannu a ciki.
Kawo yanzu dai babu cikakken bayani kan wannan batu, amma wata majiya da ta ambaci wani jami'in Faransa da ke da dangantaka da ofishin jakadancin Kamaru yace suna kyautata zaton an ɗauke su daga Kamaru ne an shigar da su Najeriya.
To sai dai a waje guda kuma lokacin wani jawabi da yayi a ƙasar Girka, shugaban ƙasar Faransa Francois Hollande ya gargadi 'yan asalin Faransar da ke yankin da su guji nuna kansu.
Mawallafiya: Pinaɗo Abdu Waba
Edita: Zainab Mohammed Abubakar