1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Garkuwa da wasu 'yan Faransa a Kamaru

February 19, 2013

Wasu da ba'a san ko su wanene ba sun yi garkuwa da wasu 'yan Faransa masu yawon buɗe ido a Kamaru

https://p.dw.com/p/17hUQ
French President Francois Hollande arrives at the EU Headquarters on February 7, 2013 in Brussels, on the first day of a two-day European Union leaders summit. European Union leaders head into a fresh clash over the EU's budget with the only certainty being that proposals for several years will be cut back. AFP PHOTO / GEORGES GOBET (Photo credit should read GEORGES GOBET/AFP/Getty Images)
Hoto: Getty Images

Rahotanni sun ce a yankin arewacin kamaru, an yi garkuwa da wani Iyalin Faransawa bakwai a ciki har da ƙananan yara guda huɗu, inda kamfanin dillancin labarun Associated Press ya rawaito cewa wasu jami'ai na zargin ƙungiyar Boko Haram da hannu a ciki.

Kawo yanzu dai babu cikakken bayani kan wannan batu, amma wata majiya da ta ambaci wani jami'in Faransa da ke da dangantaka da ofishin jakadancin Kamaru yace suna kyautata zaton an ɗauke su daga Kamaru ne an shigar da su Najeriya.

To sai dai a waje guda kuma lokacin wani jawabi da yayi a ƙasar Girka, shugaban ƙasar Faransa Francois Hollande ya gargadi 'yan asalin Faransar da ke yankin da su guji nuna kansu.

Mawallafiya: Pinaɗo Abdu Waba
Edita: Zainab Mohammed Abubakar