1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gasar kofin zakarun nahiyar Afirka

Suleiman Babayo
April 18, 2017

Kungiyar Mbabane Swallows daga Swaziland ta samu nasara ban-mamaki kan kungiyar AC Leopards ta kasar Kwango, a gaba daya da ci 4 da 3

https://p.dw.com/p/2bObk
African Cup of Nations Ägypten gegen Kamerun
Hoto: Reuters/A. Abdallah Dalsh

Kuma da wannan nasara Mbabane Swallows ta zama wata kungiya ta farko daga Swaziland da ta kai wannan mataki na gaba. Haka ita ma kungiyar Zesco Utd daga Zambiya ta samu nasara kan Enugu Rangers daga Najeriya da ci 5 da 2 a gaba daya wasannin na gida da waje.

Anata bangaren kungiyar KCCA daga Yuganda ta samu nasara bayan bugun daga kai sai mai tsaron gida a kan kungiyar Al Masry daga kasar Masar, da ci 4 da 3. Ita kuwa Mouloudia Alger daga Aljeriya ta yi sa'ar doke Young Africans daga Tanzaniya a gaba daya da ci 4 da 1.