1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ghana: Mutane 22 sun mutu wajen ginar zinari

Abdourahamane Hassane
July 7, 2017

'Yan sanda a Ghana sun ce addadin mutanen da suka mutu a cikin wata mahakar zinari ta bayan fage a kudu maso yammacin kasar sun haura daga 17 zuwa 22.

https://p.dw.com/p/2gB2n
Kinderarbeit in Goldminen - Burkina Faso
Hoto: Getty Images/AFP/A. Ouoba

Mahakar mai zurfin mita 80 wacce aka daina aiki da ita wadda kuma gwamntin ta haramta a farkon wannan shekara ta rubta da masu ginan zinarin a ranar Lahadin da ta gabata. Ghana dai ita ce kasa ta biyu a Afirka bayan Afirka ta Kudu wadda da ke da  arzikin karfen zinari, sai dai a karo da dama a kan samu irin wannan hadari.