1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gobara a China ta hallaka mutane da dama

Ahmed SalisuAugust 13, 2015

Tashin wata gobara a wani rukunin masana'antu a kasar China ya yi sandin asarar rayuka da ta dukiya mai dimbin yawa.

https://p.dw.com/p/1GEpl
China Tianjin Explosion Gefahrgutlager
Hoto: Reuters

Jami'an tsaro a kasar sun killace inda wannan lamari ya wakana a Tianjin da ke arewacin kasar kuma sun mutanen da suka jikkata sun dari hudu.

'Yan sanda sun hana jama'a musamman ma manema labarai kaiwa ga inda abun ya wakana, yayin da wasu al'ummar kasar ke zargin ana share sakonnin da suka sanya kan wannan batu a kafofin sada zumunta irinsu Twitter da Facebook.

Hotuna a shafukan intanet sun nuna yadda gobara ta yi ta'adin gaske a yankin sandiyyar fashewar wasu abubuwa da ake zaton sinadarai ne masu hadari.