1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Guinea ta fara kirga kwanakin ban kwana da Ebola

Suleiman BabayoNovember 17, 2015

Mahukuntan Guinea sun bayyana nasara kan cutar Ebola bayan an sallami mara lafiya na karshe da cutar daga asibiti.

https://p.dw.com/p/1H7O3
Sierra Leone Ebola Kinderstation Holy Spirit Hospital in Makeni
Hoto: DW/K. Gänsler

Mahukuntan kasar Guinea Conakry sun tabbatar da cewa mara lafiya na karshe dauke da cutar Ebola ta samu sauki. Yarinyar 'yar shekaru biya da haihuwa da ke karkashin kulawa an sallame ta daga asibiti a wannan Talata, abin da ke nuna shiga matakin kirga kwanaki 42, bisa tsarin hukumar lafiya ta duniya, idan babu wanda ya sake kamuwa da cutar sai a fitar da kasar daga cikin wadda take karkashin annobar cutar ta Ebola.

Cutar Ebola ta yi sanadiyar hallaka fiye da mutane dubu-11 galibi a kasashen yankin yammacin Afirka, amma da taimakon kasashen duniya aka dakile cutar. A farkon wannan wata na Nuwamba kasar Saliyo ta samu nasarar ficewa daga cikin masu dauke da cutar, tun farko Laberiya ta samu irin wannan nasara.