1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gwamnatin wuncin gadin kasar Libiya ta yi murabus

August 29, 2014

Jagoran gwamnatin wucin gadin Firaminista Abdullah al-Thani ya shaida wa majalisar dokoki ajiye aiki

https://p.dw.com/p/1D3Sy
Hoto: picture alliance/Photoshot

Gwamnatin wucin gadin kasar Libiya ta bayyana murabus bayan masu kaifin kishin addinin Islama sun kirkiro wata gwamnati. A daren wannan Alhamis da ta gabata jagoran gwamnatin wucin gadin Firaminista Abdullah al-Thani ya shaida wa majalisar dokokin murabus da gwamnati ta yi.

Saboda dalilan tsaro majalisar tana zama a garin Tobruk mai nisan kilo-mita 600 daga Tripoli babban birnin kasar. Wannan murabus da gwamnatin Libiya ta yi ya zo kwanaki uku, bayan tsohuwar majalisar dokoki ta zabi mai kishin Islama Omar al-Hassi a matsayin sabon firamnista.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Usman Shehu Usman