1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Haɗin kan ƙungiyoyin AU da EU

November 21, 2013

A taron su na shekara-shekara, kan hakkin bil adama, ƙungiyoyin AU da EU sun amince su dafa wa juna domin inganta sha'anin kiyaye hakkin ɗan adam.

https://p.dw.com/p/1AM7j
AU Commission chief Nkosazana Dlamini-Zuma speaks during an interview in the Ethiopian capital Addis Ababa on December 4, 2012. Dlamini said the African Union faced major funding constraints and should turn to 'non-traditional' backers and not rely on states' membership fees alone. 'We need to mobilise business people on the continent and beyond and financial institutions to invest in the continent, to do business in the continent,' she said. The AU, traditionally funded by annual fees from member states, lost one of its major bankrollers last year with the death of Libya's Moamer Kadhafi. The annual budget for 2013 is 278 million US dollars. AFP PHOTO / Mulugeta AYENE (Photo credit should read Mulugeta Ayene/AFP/Getty Images)
Nkosazana Dlamini-Zuma shugabar majalisar zartarwar AUHoto: Mulugeta Ayene/AFP/Getty Images

Ƙungiyar Gamayyar ƙasashen Afirka, da Ƙungiyar Tarayyar Turai sun gudanar da tattaunawarsu ta shekara-shekara a birnin Brussels, inda sukan duba batutuwan da suka shafi hakkin bil adama a nahiyoyin biyu. A wannan karon sun gano cewa duk da ci-gaban da ake samu a wasu mahimman fannoni har yanzu akwai ƙalubale, musamman a Turai, inda ake zargin rashin mutunta hakkokin masu gudun hijira da masu neman mafaka ta siyasa.

Ƙungiyar kare hakkin bil adama ta Human Rights Watch, wadda ita ma ta kasance a taron, ta nuna damuwarta dangane da rashin mutunta masu fafutukar kare hakkin jama'a a nahiyar Afirka, da take hakkokin jama'a da hana wa jama'a walwalar tarayya ko kuma ma'ammala da waɗanda suke so su yi, A Turai kuma mutunta hakkokin masu gudun hijira.

Matsalolin kare hakkin bil adama a Turai

Ko da shi ke, tun kafin gudanar da taron nasu, aka gudanar da wata zama ta fararen hula wanda ya dadale wasu mahimman matsaloli kamar yadda darektan ƙungiyar kare haƙƙin bil adama na shiyar Afirka, Baniel Bekele ya bayyana:

"A tattaunawar da fararen hula suka yi kafin zaman ƙungiyoyin biyu, sun nuna damuwa kan rashin mutunta hakkin ɗan adam, da ma irin barazana da cin zarafin da masu fafutukan kare hakkin ɗan adam, 'yan jarida da ƙungiyoyin fararen hula ke fuskanta, da ma yadda amfani da dokokin ƙasa da manufofi wajen musgunawa jama'a ke ƙaruwa, wanda kuma ke hana fararen hula gudanar da ayyukansu yadda ya kamata"

Dangane da yadda matsalar ta shafi Turan kuwa, ƙungiyoyin fararen hulan sun yi kira ga majalisun zartarwar ƙungiyoyin da su samar da manufofin da zasu yi la'akari da hakkin bil adama.

Herman Van Rompuy, President of the European Council. Ort / Datum: The 2013 Innovation Summit, 10 October 2013, Brussels. Copyright: Courtesy of @mbargo. Geliefert von James Panichi (freiberuflicher Korrespondent, Brussel) - via Chrysoula Mitta, The Lisbon Council
Herman Van Rompuy shugaban majalisar zartarwar EUHoto: Courtesy of @mbargo

Musgunawa 'yan jarida da ƙungiyoyin fararen hula

Ƙungiyar ta Human Rights Watch ta kuma yi kira ga ƙungiyoyin na AU da EU da su mayar da hankali wajen shawo kan matsalolin da kafofin yaɗa labarai ke fuskanta daga ƙasashen su Darektan ƙungiyar a yankin Afirka, Daniel Bekele ya yi ƙarin haske:

"Batu ne mai sarƙaƙiya, kuma ba wannan ne karon farko da ake tayar da wannan batu, kuma matakin da ya dace a ɗauka shi ne kwaskware wasu daga cikin dokokin dake da tsaurin gaske, waɗanda ke takurawa kafofin yaɗ labarai masu zaman kansu a Turai da Afirka, musamman ma a Afirka, saboda ƙaruwar da muke gani a Afirka, kwanan nan ne muka ga inda gwamnatoci suka fara amfani da dokokin dake hana kafofin yaɗa labarai masu zaman kansu da ƙungiyoyin fararen hula gudanar da ayyukansu yadda ya kamata."

Bundeskanzlerin Angela Merkel (CDU, l) und die Vorsitzende der Afrikanischen Union (AU), Nkosazana Dlamini-Zuma, geben sich am 11.07.2013 im Kanzleramt in Berlin nach einer gemeinsamen Pressekonferenz die Hand. Foto: Soeren Stache/dpa +++(c) dpa - Bildfunk+++
Shugabar gwamnatin Jamus da Dlamini Nkosazana ZumaHoto: picture-alliance/dpa

Manufofin ƙasashen Turai masu tsauri

Yawancin waɗanda ke gudun hijira suna guduwa ne daga ƙasashen da ke fama da gwamnatoci masu mulkin danniya, kuma har wa yau wasunsu mutane ne da ke fiskantar barazana daga mahukuntan ƙasar, to ko ta yaya ƙungiyar kare haƙƙin bil adaman ke ganin cewa ƙungiyar ta EU zata taimaka wajen ganin cewa an ɗauki masu gudun hijira.

"Manufofin turai kan gudun hijira musamman kan iyakokinta, sun mayar da hankali ne kan tasa ƙeyar 'yan gudun hijira da fararen hula, maimakon ceton rayukan mutane musamman kan teku, saboda haka mun yi kira ga ƙasashen Turai da su ba da mahimmanci wajen mutunta rayukan jama'a a maimakon ɗaukaka dokar su ta kula da kan iyaka, su ceto mutanen da suka sami kansu cikin mawuyacin hali, domin ganin an kai su ƙasar Turan da ya fi kusa da inda suke a ba su matsugunni maimakon sanya fifiƙo kan tsaron kan iyaka.A ƙarshe dai ƙungiyoyin sun cimma matsayar ɗaukar matakan da zasu taimaka wajen samar da cigaba mai ma'ana.

Mawallafiya: Pinaɗo Abdu Waba
Edita: Abdourahamane Hassane