1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Habaka tattalin arzikin Afirka da na Larabawa

November 19, 2013

Afirka da kasashen Larabawa za su daddale hanyoyin karfafa huldar tattalin arziki a tsakaninsu.

https://p.dw.com/p/1AKZ0
GettyImages 169454551 A general view shows delegates attending the 50th African Union Aniversary Summit in Addis Ababa on May 25,2013. Today's 54-member AU is the successor of the Organisation of African Unity (OAU), established amid the heady days as independence from colonial rule swept the continent in 1963. AFP PHOTO/SIMON MAINA (Photo credit should read SIMON MAINA/AFP/Getty Images)
Hoto: AFP/Getty Images

A wannan Talatar (19. 11. 13) ce kasashen Afirka da na Larabawa ke bude taron koli na yini biyu a kasar Kuwait domin bitar matakan da suka dauka na karfafa huldar tattalin arziki a tsakanin kasashen yankin tekun Fasha da ke da karfin tattalin arziki da kuma zuba jarinsu a nahiyar ta Afirka. Wannan taron dai shi ne zai kasance mafi girma irinsa na farko tun bayan wanda ya gudana a shekara ta 2010, yayin da shugabannin sassan biyu suka gana a kasar Libiya, gabannin juyin juya halin kasashen Larabawa, wanda yayi awon gaba da mai masaukin bakinsu a wancan lokacin, wato marigayi shugaba Ghaddafi da kuma wasu takwarorinsa a wasu kasashen arewacin Afirka da kuma na yankin Gabas Ta Tsakiya. Ana dai sa ran shugabannin kasashe 23 da kuma mataimakan shugabanni bakwai, game da shugabannin gwamnatoci uku ne za su halarci taron kolin, wanda ke da nufin karfafa harkokin tattalin arziki a tsakanin yankunan biyu.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Umaru Aliyu