1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jirgin Ethiopian airlines na kasar Habasha ya yi hatsari

Abdoulaye Mamane Amadou MA
March 10, 2019

Ba ko daya da ya tsira daga cikin fasinjoji 157 da ke cikin jirgin saman Habasha Ethiopian airlines da ya yi hatsari a ranar Lahadi da safe kan hanyarsa ta zuwa Nairobi Kenya.

https://p.dw.com/p/3EjoL
Äthiopien Mehr als 150 Tote bei Flugzeugabsturz
Daya daga cikin tarkacen jirgin saman Habasha da ya fadiHoto: Reuters/T. Negeri

'Yan kasar kenya na kan gaba a jerin 'yan kasashen wajen da suka hallaka sakamakon hatsarin jirgin saman kamfanin Habasha na Ethiopian airlines. Kasashen 32 ne lamarin ya shafa da suka hada da 'yan Kanada (18) 'yan Habasha (9) 'yan Italiya (8) China (8)  Amirka (8) Birtaniya (7) Faransa (7) Nerland (5) Indiya (4) sai ma'aikatan Majalisar Dinkin Duniya 4.

 Kamfanin Ethiopian airlines mallakar kasar ta Habasha ya ce tuni ya aike da tawagar ma'aikatansa da za su taimakawa masu bayar da agaji a yankin Bishoftu  na Oromo da ke kudancin kasar  wurin da jirgin ya yi hadarin, to amma sai dai kamfanin ya ce ba wanda ya tsira da ransa kawo yanzu daga faduwar jirgin. 
 
Tuni dai Firaministan kasar Abiy Ahmed, da Shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyatta suka wallafa sakon juyayi da kuma jaje ga iyalan wadanda aka rasa a hatsarin. Ita ma dai kungiyar Tarayyar Afirka ta bakin shugabanta Moussa Faki Mahammat ya aikewa iyyalan wadanda hatsarin ya rutsa da su sakon ta'aziya.