1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tuhumar 'yan adawa a Kongo

Gazali Abdou TasawaMay 19, 2016

Wata kotu a birnin Kinshasa ta tuhumi jagoran adawa a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kongo, wanda kuma ya tsaya takarar shugabancin kasar Moise Katumbi da aikata laifin cin amanar kasa.

https://p.dw.com/p/1IqrW
Moise Katumbi Chapwe Kongo
Hoto: Getty Images/F. Scoppa

Babban lauyan gwamnatin kasar ne dai ya bayyana wannan tuhuma a wani zama da kotun ta yi a wannan Alhamis, wanda ke zaman mataki na karshe na sauraren karar da gwamnatin ta shigar kan dan adawar kafin soma zaman shari'ar na gadan-gadan kan batun nasa. Idan dai har kotun ta same shi da aikata wannan laifi na zargin cin amanar kasa, to kuwa tana iya yanke masa hukuncin zaman gidan kaso na daurin rai da rai .

A hannu guda kuma gwamnatin kasar ta bada sammacin kamo Moise Katumbi a bisa zargin daukar sojojin haya a jihar Katanga inda ya rike mukamin gwamna daga shekara ta 2007 zuwa ta 2015. Wasu na kusa da Moise Katumbin dai sun ce a halin yanzu Katumb na akwance a wani asibiti na birnin Lubumbashi da ke Kudu maso Gabashin kasar.