1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hamas ta nemi a fita intifada ranar Juma'a

Yusuf Bala Nayaya
December 7, 2017

An dai shiga fargaba tun bayan da Trump ya ce Birnin Kudus ya zama babban birnin Isra'ila yayin da Falasdinawa suka ce babban birninsu ne.

https://p.dw.com/p/2ozA2
Gaza - PK von Hamas-Chef Ismail Haniyeh wegen Jerusalem-Status
Hoto: Reuters/M. Salem

An dai shiga zanga-zanga a yankin Falasdinawa bayan da Shugaba Donald Trump na Amirka ya bayyana birnin Kudus a matsayin babban birnin Isra'ila. Shugaban kasar Turkiya Tayyip Erdogan da Fafaroma Francis sun amince a wata tattaunawa ta wayar tarho a wannan rana ta Alhamis cewa duk wani kokari na sauya matsayar Birnin Kudus abu ne da ya kamata a kauce masa kamar yadda ofishin Erdogan ya bayyana.

A cewar majiyar labarin dukkanin shugabannin biyu Erdogan da Fafaroma sun amince cewa birnin Kudus waje na ibada mai tsarki ne da mabiyan addinin Musulinci da Kirista da ma mabiya na addinin Yahudu. Tuni dai kungiyar Hamas ta sha alwashi na fita intifada a karo na uku a ranar Juma'a abin da ke haifar da fargabar kwarara ta jini da rasa rayuka.